Posts

YAWAN 'DAUKAKA LAIFI DA MA'AURATA KE YI YA FI KOMAI HADDASA SAKIN AURE- Azeeza Idris

Image
Azeeza Idris  wacce aka fi sani da Ummyasmeen  musamman a kafar sadarwa ta Instagram da kafar karanta littatafai ta duniyar gizo wato Wattpad. Marubuciya ce da tauraronta ke haskawa saboda d’umbin fikrar da Allah ya ba ta. Ta ci sarauniyar Marubuta Nigeria a Duniyar Wattpad sannan tana da dubban Makaranta littafanta daga ko ina a fad’in duniyar nan. Ba a rubutu kad’ai ta shahara ba har ma da fannin girke-girke. Ga hirarta da Mujallar Fikra.. Mujallar Fikra:          Assalamu Alaikum warahmatullah Aziza Idris :               Wa’alaikumus salam Wa Rahmatullah Mujallar Fikra:         Za mu so sanin wacece Umm Yasmeen Aziza Idris :               Masha Allah, da farko dai sunana Azizah Idris Muhammad. An haife ni a jihar Bauchi a ranar 06/10/1988. Amma ni asali 'yar jihar Gombe ce daga karamar hukumar Yamaltu/Deba.  Nayi karatun  firama...

Marubuci idon al'umma ~ Ummu-Abdoul

Image
MARUBUCI IDON AL'UMMA Safiyyah Ummu-Abdoul safiyyahjibril@gmail.com Al'umma kan k'aru ta fannoni da dama daga Alkalamin marabuci. Mai rubutu ba zai kasance marubuci ba har sai ya kasance ido ga al'umma  idon da ba makauniyar ido ba. Yana da kyau kafin ka fara rubutu ka yi tunanin shin shahara kake nema a wajen al'umma ko kuma shahara kake nema a wajen Ubangijinka. Sau da yawa marubuta kan manta cewa yanda rubutun su kan samar musu soyayya a idon jama'a hakan zai iya sama musu soyayyar Allah har ta zama sanadin shigar su Aljanna. Amma kuma hakan ba yana nufin shi marubuci malami ne ta fuskar addini ba, hakan ba zai sa ya zama masanin kimiyyar siyasa ko tattalin arziki ba da har zai ga ai yana da lasisin yanke hukunci ta wannan fannin matukar ba ya kasance mai ilimi akan wannan fannin ba. Kasancewar ka idon Al'umma hakan bai sa dole duk abin da ya fito daga bakinka ya zama shi ne daidai ba da har dole in ba'a bi ra'ayin ka ba toh mutane sun ɓata. ...

YA KAMATA GWAMNATOCIN AREWA SU TALLAFA WA RUBUTU DA MARUBUTA HAUSA ~ AUYO

Image
Auyo matashin marubuci ne da yayi tashe a lokacinsa, salon rubutunsa ya sha bambam da rubutun mafi akasarin Marubuta. ya fara rubutu tun yana da shekara goma sha uku a duniya kuma har ila yau yana rubutu mai cike da fad'akarwa, ilmantarwa gami da Nishad'antarwa. Littafinsa HISABI na d'aya daga cikin tarin littafan da Makaranta ke tsumaye. Ga hirarsa da Mujallar Fikra *** Mujallar Fikra :             Assalamu Alaikum warahmatullah Auyo :                            Waalaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu Mujallar Fikra :            Zamu so mu ji takaitaccen tarihinka   Auyo :                       Cikakken sunana Abubakar Muhammad . An haife Ni a garin Auyon Jiha...

AURE BAUTAR ALLAH CE BA BAUTAR MIJI BA

Image
Daya daga cikin matsalolin aure a Nahiyar Afirka Shine ɗaukan aure a matsayin bautar Miji tun da hadisi ya zo akan Aljannar mace yana karkashin kafar mijinta maimakon su yi amfani da kasancewar sa tsani zuwa ga  Aljanna ta hanyar kyautata masa don samun yardan Allah Da ace iyaye suna faɗakar da ya'yansu Mahimmancin yin komai da ya shafi zamantakewar aure a matsayin ibada da mazaje ba za su cutar da matan da suka aura ba sannan mata ba zasu gaji da yi ma mazajen su biyayya ba saboda ban taɓa jin an ce an gaji da yi ma ALLAH biyayya ba. Yana daga cikin Al'adunmu in za'a aurar da mace ayi ta kira mata hakuri, ni a gani na ba hakuri kawai ya kamata a kira mata ba sai a kara da ta ji tsoron Allah sannan ki nemi yardan Allah. Don abubuwa ukun nan shine sirrin zaman lafiya a gidan aure. Bayan kalmar Hakuri da ake ambata mata sai kuma cusa ma yarinyar ra'ayin in ba ta bi mijinta ba zai sake ta, ko zai kara aure ko kuma zai bi kadangarun bariki,  abin mamaki kuma sai ...