YAWAN 'DAUKAKA LAIFI DA MA'AURATA KE YI YA FI KOMAI HADDASA SAKIN AURE- Azeeza Idris
Azeeza Idris wacce aka fi sani da Ummyasmeen musamman a kafar sadarwa ta Instagram da kafar karanta littatafai ta duniyar gizo wato Wattpad. Marubuciya ce da tauraronta ke haskawa saboda d’umbin fikrar da Allah ya ba ta. Ta ci sarauniyar Marubuta Nigeria a Duniyar Wattpad sannan tana da dubban Makaranta littafanta daga ko ina a fad’in duniyar nan. Ba a rubutu kad’ai ta shahara ba har ma da fannin girke-girke. Ga hirarta da Mujallar Fikra.. Mujallar Fikra: Assalamu Alaikum warahmatullah Aziza Idris : Wa’alaikumus salam Wa Rahmatullah Mujallar Fikra: Za mu so sanin wacece Umm Yasmeen Aziza Idris : Masha Allah, da farko dai sunana Azizah Idris Muhammad. An haife ni a jihar Bauchi a ranar 06/10/1988. Amma ni asali 'yar jihar Gombe ce daga karamar hukumar Yamaltu/Deba. Nayi karatun firama...